Posts

Showing posts from April, 2021

Bayani kan Zamantakewar aure A Kasar Hausa

Image
A zamantakewar aure, miji da mata suna da hakkoki da kowannensu ya kamata ya kiyaye. Abu na farko da ya kamata ma’aurata su sani shi ne: Allah ne Ya halicce su daga rai guda, wato annabi Adamu, sannan Ya halicci matarsa Hauwa’u daga gare shi domin samun natsuwa, to hakkin Allah a nan shi ne su bauta maSa Shi kadai ba tare da gwamutsa wani abu ba wajen bautar. Wannan ya hada da dukan sauran abubuwan da imani da Allah ya kunsa. Bayan wannan ya kamata ma’aurata su san hakkokin da ke kansu, su fahimci mene ne shari’a ta dora wa kowannensu. Zaman aure wani abu ne da ake fatan daga lokacin da aka fara tunaninsa ya zamo wani abu na mutu-ka-raba, domin hakan ne zai tabbatar da cewa an san abin da ake nufi da aure da kuma irin halin da za a shiga. Sanin hakkokin da ke kanka a matsayin miji, sanin matsayinki na mata a gidan aure yana da mahimmancin gaske, domin hakan ne zai ba da damar tabbatar da wanzuwar wannan aure. Yana da kyau ma’aurata su sani, aure ba tsari ne na zama zuwa wani dan lokaci...

Hakki Ne Hausa Novels Complete

Image
  HAK'K'I NE            ( *NEMESIS*) _Ummu Asma'u(sa'adatu) *Bismillahirahamanirrahim* Godiya ta tabbata ga Allah (SAW), Alhamdulilahi, ina godiya ga dukanin masoyana, na gode maku sosai. Nah sadaukar da wanan littafin mai suna *HAK'K'INE* Ga Mahaifana, Allah yayi maku Rahama. Wanen labarin Kirk'iraren labari ne, banyi don wani ko wata ba. *page* 1⚜2 A garin *MISAU* a jihar Bauchi, a unguwar central layin makama, cikin wani kyakyawan gida mai kyan tsari, wasu kyawawan fararen 'yan mata ne suka yi sallama suka shigo cikin falon. Wata kyakkyawar mace fara sosai irin farin nan na ainihin fulanin asali ce  ta amsa sallamar 'yan matan, cikin jin dad'in ganin su tace har an taso makarantar. Wadda tafi girman tace mun taso Aunty sannu da gida, matar da suka kira Aunty tace sannunku, me ya samu Auta ta? Ummi da tun shigowar su falon ita ke magana, tace ita da yan ajin su  ne, maganar ko yaushe,  wai babanta mai kudi ne amma  muna makarantar...